Adashen Ƙauna 5 - Barka da Salla


    Na tsara waɗannan ‘yan baitoci ne a matsayin barka da salla ga A’isha (Humaira). Bayan shauƙin soyayya da ya ja ni zuwa ga tunanin baitukan, a ɓangare guda shauƙin adabi da ke zuciyata ya taimaka wajen ingizo mini jeranton kalaman da zan yi rubdugun salailai da su. A bisa wannan dalili, bayan kasancewar ‘yan baitocin saƙon soyayya, suna zaman wata maƙera ta sarrafa harshe da luguden kalmomi. A taƙaice, an ƙuduri jifan tsuntsaye biyu ne da dutse guda.



    1. Hamdan Allah Rahimi,
    Baiwar da ka min rai yai fari.

    2. Ka ƙaran basira zuciya,
    Ninkinta ya zam wane ɗari.

    3. Ka ƙara salati Rabbana,
    Ga manzon tsira ɗahiri.

    4. Alaye da sahabu sa-
                Dukanmu masoya zikiri.

    5. Humaira ƙalamna ke nufi,
    Da na bayyana son ta a sarari.

    6. Hotonki na salla ya iso,
    Abin da ido ke marrari.

    7. Sun zaga ƙwaƙwalwa tai yabo,
    Ganinsu ya sa zuci marmari.

    8. A kullum ina daɗa godiya,
    Ilahu ya ban damar ciri.

    9. Na banke maza da guda-guda,
    Da kowa ke faman hari.

    10. Samunki ya sa na wuce maza,
    Kaɗan ya hana mini fahari.

    11. Son da nake miki ya cika,
    Yawansa ya kai ai nazzari.

    12. Zan so ki da baki da zuciya,
    In ɗauke ki mu zaga gari-gari.

    13. Duk matsalarki fada mini,
    In saurare ki da hamzari.

    14. Son da nake miki baɗini,
                Tuni ya ninka na zahiri

    15. Son da nake miki A'isha,
    Girmansa ya wuce nazari.

    16. Ya riƙa yai tozo ƙaho,
    Na ga son har ya yo ƙari.

    17. Ƙarinsa na harbe mahassada,
    Da mai gulmar mu da makiri.

    18. Humaira son ki ya kumbura,
    Zuciya ta cika ba wuri,

    19. An ce ƙuncin zuciya,
    Cuta ce da ba ta da makkari,

    20. Ni na samo magani,
    Humaira ke ce sinadari.

    21. Ash'ab ba ni da walwala,
    Son ki ya saka mini sasari.

    22. Walwalata guda sai in da ke,
    Zumuɗi har da su mazzari.

    23. Idan ba kya kusa ban nitso,
    Kamar na hau borin giri.

    24. Riƙe ni in samo nitsuwa,
    Kada sonki ya sa a sakan mari.

    25. Kallonki ne 'yancin zuciya,
    Da ke kulle ta dawo sarrari.

    26. Na so ki, ki so ni mu yo ta so,
    A sonki na ƙaro kuzzari.

    27. Na shirya, shirya mu je,
    Shirinmu kar ya yi jinkiri.

    28. Riƙen in riƙe ki mu zam guda,
    Riƙon mu yi ƙamƙam ya maƙari.

    29. Tsaya in tsaya mu yi tsaitsaye,
    Mu tsare matsalar duk mai hari.

    30. Ki zo na zo mu zamo haɗe,
    Zamanmu ya zam zakkar gari.

    31. Ki shigo na shigo mu shige ciki,
    Shigarmu cikin nai wa shiri.

    32. Miƙo na miƙe mu miƙa gaba,
    A gano mimmiƙarmu a sarari.

    33. Doso na doso mu doshi-
    Zamanmu da ba rabuwa har kakari.

    34. Hanga na hango mu hangi-
    Zaman da masoya duka ke hari.

    35. Abu ga Ubaida yake batu,
    Na Humaira masoyin zahiri.

    36. Barka da salla kau na yi,
    Cikin zantukanga ƙiri-ƙiri.

    Pages